Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ra’ayoyin Ma’abota VOA Hausa Kan Cikar Sashen Shekaru 45


VOA Hausa shekaru 45
VOA Hausa shekaru 45

Ma’abota sauraron Sashen Hausa na Muryar Amurka na ci gaba da bayyana ra'ayoyin su kan cikar sashen shekaru 45 da fara aiki.

ABUJA, NIGERIA - Cikin shekarun nan Sashen ya shahara wajen yada shirye-shirye da labaru masu ilimantarwa, fadakarwa harma da nishadantarwa, daga siyasa, lafiya, ilimi, shari’a, tattalin arziki da sauran su.

‘Yan siyasa da jami’an gwamnati dama kungiyoyi suna ta fadan ra’ayinsu.

Sanata Adamu Aliero ya ce VOA Hausa ta yi fice wajen wayar da kan jama'a kan sanin 'yancin su.

Shima Shugaban kungiyar muryar talaka Zaidu Bala Kofa Sabuwa ya ce ya shafe fiye da shekaru 20 ya na hulda da Sashen da ya zama masa tamkar makaranta; ya na mai addu’ar rahama ga wadanda suka rasu.

A na ta sharhin Zainab Muhammad Bununu ta ce Sashen ya taka rawar gani wajen wayar da kan mata musamman a bangaren siyasa.

Mai sauraron Muryar Amurka a yankin karkara Sulaiman Magama Gumau ya ce tashar ce ke kan gaba wajen wayar da al'ummar arewacin Najeriya.

A Najeriya da sanyin safiya za ka ga masu sauraro da ke shirin fita ayyukan yau da kullum su na sauraron shirin farko na kafar labarun ta duniya da karfe 6.00 don sanin halin da duniyar ke ciki.

Saurari cikakken rahotonr:

Ra’ayoyin Ma’abota VOA Hausa Akan Cikar Sashen Shekaru 45 .mp3
please wait

No media source currently available

0:00 0:05:22 0:00

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG