Wasu ‘yan bindiga daga kungiyoyin miyagu sun kashe mutane 25 a lokacin da suka kai farmaki a wasu kauyuka hudu a yankin arewa maso yammacin Najeriya, a matsayin ramuwar gayya saboda farmakin da sojoji suka kai maboyarsu, a cewar wani jami’in tsaro a yankin.