A cewar NELFUND, dalibai zasu neman rance domin cimma burinsu na karatu ba tare da wata matsala ba.
Ministar Mata, Uju Kennedy -Ohanenye, ta janye karar da ta shigar a kan kakakin majalisar dokokin jihar Niger, Abdulmalik Sarkindaji, akan aniyar sa ta auren marayu 100 daga mazabarsa.
A cewar Hukumar EFCC mai yaki da masu yiwa tattalin arzikin Najeriya ta’annati, an gurfanar da ‘yan Chinar ne a ranar Litinin 22 ga watan Afrilun daya gabata tare da kamfaninsu mai suna, Ebuy Concept Limited, akan tuhuma guda dake da nasaba da hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba.
Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta hana bada belin Tigran Gambaryan, babban jami’in kamfanin hada-hadar Kudi ta Yanar gizo Binance.
Kafaffen yada labaran cikin kasar Najeriya sun ruwaito cewar Shugaban na Sengal ya zo ziyarar aiki a Najeriya ne.
Ana zargin wani matashi, Shafi'u Abubakar, wadda aka ruwaito cewar, ya bayyana wata dadaddiyar takaddamar rabon gado a matsayin dalilinsa na haddasa fashewar.
A daidai lokacin da duniya ke komawa fannin amfani da iskar gas don rage illolin sauyin yanayi ga al’umma, gwamnatin Najeriya ta kaddamar da muhimman ayyukan samar da iskar gas guda uku a jihohin Imo da Delta.
Shugaban Kungiyar Kwadago ta NLC, Joe Ajero, ya bayyana cewar ba da gaske gwamnatin tarayyar take ba a tattaunawarta da 'yan kwadagon game da sabon mafi karancin albashi.
Domin Kari
No media source currently available
Amurkawa za su yi zabe a watan Nuwamba, batutuwan da suka shafi Afirka ba su dame su sosai ba. Sai dai masu sharhi na ganin duk wanda ya yi nasara a zaben, yana da jan aiki na dawowa kimar Amurka a nahiyar ta Afirka.
Wani matashi a garin Larabar Abasawa dake karamar hukumar Gezawa ya cinnawa wani masallaci wuta yayin da mutane suke sallar asubahi. Rundunar ‘yan sadan jihar ta ce mutumin ya zuba fetur ne, ya banka wuta, sannan ya rufe kofar masallacin. Kimanin mutane 35 ne suka samu raunukan sakamakon al'amarin.
Bayan kawancen soji dake tsakanin kasashen biyu, a yanzu haka kasar ta Rasha ta bullo da wani sabon tsari na koyar da harshen kasarta a makaratun Nijar. Yayin da wasu ‘yan Nijar ke alfahari da shirin, wasu kuwa jan hankalin hukumomin kasar suke yi a game da matsalar da za a iya samu.
Ma’aunin matsalar cin hanci da rashawa a Zambia ya nuna cewa kasar ta samu ci gaba a karon farko cikin shekaru goma, kamar yadda kungiyar Transparency International a kasar ta sanar. Hukumomi a kasar sun ce kwalliya ta fara biyan kudin sabulu a dagewar da suka yi wajen karfafa bin doka da oda.
A lokacin da Martha Ngoye take aiki a matsayin babbar jami’ar al’amuran shari’a a hukumar sufurin jiragen kasa ta Afirka ta Kudu, ta kwarmata badakalar kwangilolin gwamnati na miliyoyin kudi da aka bayar ba bisa ka’ida ba. Sai dai a maimakon a sakanya mata da alheri, sai aka kore ta a wurin aiki.
Kungiyoyin tabbatar da ka’ida a hada-hadar tattalin arziki a Malawi sun yi kira ga gwamnatin kasar da ta magance wasu matsaloli da ke tattare da tsarin bayar da kwangiloli na kasar.Wani rahoto a 2021 ya nuna cewa harkokin bayar da kwangiloli na gwamnati a kasar suna dabaibaye da cin hanci da rashawa