Bangarorin biyu sun yanke shawarar Amurka za ta janye dakarunta cikin 'yan watannin masu zuwa ba tare da bata lokaci ba.
A ranar Alhamis gwamnatin Sudan ta Kudu da kungiyoyin 'yan tawaye suka rattaba hannu kan "yarjejeniya" samar da zaman lafiya a yayin tattaunawar neman sulhu a kasar Kenya, wanda aka bayyana a matsayin muhimmin mataki na kokarin kawo karshen rikicin Sudan ta Kudu da ya durkusar da tattalin arzikinta.
Ministan Ma’adinan jamhuriyar Benin a yayin wani ganawa da manema labarai yace kasarsa ta amince wa Nijar ta fara loda danyen man kan jirgin farko a matsayin matakin wucin gadi a bisa la’akari da yarjeniyoyin da ke tsakanin kasashen biyu.
Wata tawagar jami'an gwamnatin Amurka ta isa Jamhuriyar Nijar da daftarin da ke dauke da fasalin da Amurka ke fatan ganin an yi amfani da shi wajen kwashe dakarunta daga Nijar kamar yadda hukumomin mulkin sojan CNSP suka nuna bukata a watan Maris din da ya gabata.
Shugaban Ghanan, ya jefa wannan kalubalen ga takwarorinsa ne, a wajen bude taron koli na kwanaki uku kan kirkire-kirkire, tasiri da zuba jari, ko 3i Africa Summit a birnin Accra.
Gwamnatin rikon kwarya ta Jamhuriyar Nijar ta maida martani bayan da shugaban kasar Benin Patrice Talon ya dauki matakin hana lodin danyen man da Nijar ke shirin fara shigarwa kasuwannin duniya a tsakiyar watan Mayu.
Akalla mutum 90 aka samu tabbacin sun ji raunuka iri-iri a N’djamena, babban birnin kasar.
Alkaluman zaben sun nuna cewa Deby Itno ya samu kashi 61 cikin 100 na kuri’un da aka kada, yayin da Masra ya samu kashi 18.5 cikin 100.
Alkaluman zaben sun nuna cewa Deby Itno ya samu kashi 61 cikin 100 na kuri’un da aka kada, yayin da Masra ya samu kashi 18.5.
A cewar rahoton, adadin mutanen da zasu fuskanci matsalar karancin abinci a yankunan yammaci da tsakiyar nahiyar afirka a wannan dan tsakani zai kai kimanin mutane milyan 52 kwatankwacin kaso 12 cikin 100 na mutanen da aka tantance.
A ranar Juma’a ne likitoci a Kenya za su koma bakin aikin su, bayan sun amince da gwamnatin a kan yadda za a biya su sauran albashinsu da ya makale.
Domin Kari
No media source currently available
Ma’aunin matsalar cin hanci da rashawa a Zambia ya nuna cewa kasar ta samu ci gaba a karon farko cikin shekaru goma, kamar yadda kungiyar Transparency International a kasar ta sanar. Hukumomi a kasar sun ce kwalliya ta fara biyan kudin sabulu a dagewar da suka yi wajen karfafa bin doka da oda.
A lokacin da Martha Ngoye take aiki a matsayin babbar jami’ar al’amuran shari’a a hukumar sufurin jiragen kasa ta Afirka ta Kudu, ta kwarmata badakalar kwangilolin gwamnati na miliyoyin kudi da aka bayar ba bisa ka’ida ba. Sai dai a maimakon a sakanya mata da alheri, sai aka kore ta a wurin aiki.
Kungiyoyin tabbatar da ka’ida a hada-hadar tattalin arziki a Malawi sun yi kira ga gwamnatin kasar da ta magance wasu matsaloli da ke tattare da tsarin bayar da kwangiloli na kasar.Wani rahoto a 2021 ya nuna cewa harkokin bayar da kwangiloli na gwamnati a kasar suna dabaibaye da cin hanci da rashawa
Hukumomi a Najeriya sun daura damarar yaki da magudin zabe, a wani muhimmin lamari ga dimukradiyya a Afirka. Bayan babban zaben 2023, Najeriya ta fara daukan matakan hukunta wadanda aka samu da laifin magudin zabe domin dawo da martabar tsarin zabe a kasar.
A farkon wannan shekarar, kungiyar dake fafutukar yaki da cin hanci ta kasa da kasa, Transparency International, cikin rahotonta na 2023, ta ce yaki da matsalar cin hanci da rashawa a Afirka ya fuskanci koma-baya sosai, inda a wasu kasashen, babu wani abu da aka cimma a game da haka.
Hukumomi a Najeriya su na duba yiwuwar bullo da jami’an ‘yan sanda mallakin jihohi a fadin kasar a wani bangare na magance hare-haren ‘yan bindiga, da garkuwa da mutane da kuma ‘yan fashin daji. ‘Yan Najeriya dai sun yi maraba da wannan yunkuri, sai dai suna cike da shakku.