A cikin kwanaki masu zuwa, ana sa ran sojojin Amurka da ke gabashin tekun Bahar Rum za su hada karshen daya gefen harabar wata dirkekiyar tashar jirgin ruwa - mai tsawon filayen wasan kwallon kafa na Amurka guda biyar a gabar teku a arewacin Gaza.
Mataimakin sakataren harkokin wajen Amurka Kurt Campbell ya fada a ranar Litinin cewa gwamnatin Biden ba ta ganin akwai yuwuwar Isra’ila ta samu “cikakkiyar nasara” wajen fatattakar Hamas a yankin Gaza na Falasdinu.
Shugaba Joe Biden ya fada jiya Laraba cewa ba zai aika da muggan makamai ga Isra'ila da za ta iya amfani da su wajen kai hare-haren wuce gona da iri kan Rafah ba, wanda yake tungar karshe ta Hamas a Gaza, saboda nuna damuwa kan yadda zai afka kan fararen hula fiye da miliyan 1 da ke fakewa a wurin.
A ci gaba da shari'ar tsohon Shugaban Amurka, Donald Trump, wadda ake yi a New York, tauraruwar fina finan batsa, Stormy Daniels, ta yi bayani mai cike da batsa jiya a kotun.
Duk da cijewar da tattaunawar Isira'ila da Hamas ta yi, Amurka na fatan bangarorin biyu za su cimma jituwa kan sauran bambancin da ke tsakaninsu don a samu tsagaita wuta.
Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya tashi daga Abuja zuwa birnin Dallas na kasar Amurka, domin wakiltar shugaba Bola Tinubu a taron kasuwanci na Amurka da Afirka na 2024 wanda kungiyar kamfanoni kan Afirka ta shirya.
Mutanen 19 da suka fito daga rukuni daban-daban da shugaban Amurka Joe Biden ya karrama a ranar Juma'a saboda yin abin da Fadar White House ta kira a tsayin wadanda suka taka muhimmiyar rawa wajen bada gudunmawa a bangarori daban-daban, da tsaron Amurka da wasu muhimman ayyuka ga al'umma.
Amurka za ta bayar da kusan dala miliyan 55 don magance matsalar jin-kai a Burkina Faso, in ji jami’ar bayar da agaji ta Amurka Samantha Power a ranar Alhamis, a cewar wata sanarwa da Kamfanin Dillancin Labarai na Reuters ya gani.
A ranar Talata ne aka yanke wa Changpeng Zhao, tsohon shugaban kamfanin Binance, hukuncin zaman gidan yari na tsawon watanni hudu, bayan da ya amsa laifinsa na keta dokokin Amurka kan safarar kudade a babbar kasuwar hada-hadar kudi ta duniya.
Sojojin kasar Mali sun kashe Abu Huzeifa, kwamandan kungiyar Da'ish a yammacin Afirka, a wani gagarumin farmaki da suka kai a yankin Menaka da ke arewacin kasar, a cewar sanarwar da hukumomin Malin suka karanta a gidan talabijin din kasar a ranar Litinin din nan.
Cikin wata sanarwar hadin gwiwa da gwamnatocin Burtaniya da Amurka suka fitar ta yi Allah wa dai da kashe-kashen fararen hula da aka yi a kasar Burkina Faso.
Yarima Harry da matarsa Meghan za su ziyarci Najeriya a watan Mayu don tattaunawa kan wasannin Invictus, wanda ya kirkira don taimakawa tsoffin sojoji da wadanda ke kan aiki masu raunuka don su samu lafiya, in ji wani jami'in Najeriya a ranar Lahadi.
Domin Kari
No media source currently available
Ma’aunin matsalar cin hanci da rashawa a Zambia ya nuna cewa kasar ta samu ci gaba a karon farko cikin shekaru goma, kamar yadda kungiyar Transparency International a kasar ta sanar. Hukumomi a kasar sun ce kwalliya ta fara biyan kudin sabulu a dagewar da suka yi wajen karfafa bin doka da oda.
A lokacin da Martha Ngoye take aiki a matsayin babbar jami’ar al’amuran shari’a a hukumar sufurin jiragen kasa ta Afirka ta Kudu, ta kwarmata badakalar kwangilolin gwamnati na miliyoyin kudi da aka bayar ba bisa ka’ida ba. Sai dai a maimakon a sakanya mata da alheri, sai aka kore ta a wurin aiki.
Kungiyoyin tabbatar da ka’ida a hada-hadar tattalin arziki a Malawi sun yi kira ga gwamnatin kasar da ta magance wasu matsaloli da ke tattare da tsarin bayar da kwangiloli na kasar.Wani rahoto a 2021 ya nuna cewa harkokin bayar da kwangiloli na gwamnati a kasar suna dabaibaye da cin hanci da rashawa
Hukumomi a Najeriya sun daura damarar yaki da magudin zabe, a wani muhimmin lamari ga dimukradiyya a Afirka. Bayan babban zaben 2023, Najeriya ta fara daukan matakan hukunta wadanda aka samu da laifin magudin zabe domin dawo da martabar tsarin zabe a kasar.
A farkon wannan shekarar, kungiyar dake fafutukar yaki da cin hanci ta kasa da kasa, Transparency International, cikin rahotonta na 2023, ta ce yaki da matsalar cin hanci da rashawa a Afirka ya fuskanci koma-baya sosai, inda a wasu kasashen, babu wani abu da aka cimma a game da haka.
Hukumomi a Najeriya su na duba yiwuwar bullo da jami’an ‘yan sanda mallakin jihohi a fadin kasar a wani bangare na magance hare-haren ‘yan bindiga, da garkuwa da mutane da kuma ‘yan fashin daji. ‘Yan Najeriya dai sun yi maraba da wannan yunkuri, sai dai suna cike da shakku.